Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 25:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ibrahim ya auro wata mace kuma, sunanta Ketura.

2. Ta haifa masa Zimran, da Yokshan, da Medan, da Madayana, da Yisbak, da Shuwa.

3. Yokshan ya haifi Sheba da Dedan. 'Ya'yan Dedan su ne Asshurim, da Letushim, da Le'umomim.

4. 'Ya'yan Madayana su ne Efa, da Efer, da Hanok, da Abida, da Eldaya. Waɗannan duka 'ya'yan Ketura ne.

5. Ibrahim ya ba Ishaku dukan abin da yake da shi.

6. Amma ga 'ya'yan ƙwaraƙwarai Ibrahim ya ba da kyautai, ya sallame su tun yana da rai, su tafi nesa da Ishaku zuwa can cikin ƙasar gabas.

7. Waɗannan su ne kwanakin shekarun Ibrahim a duniya, shekara ɗari da saba'in da biyar.

Karanta cikakken babi Far 25