Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 24:62-67 Littafi Mai Tsarki (HAU)

62. A lokacin kuwa Ishaku ya riga ya zo daga Biyer-lahai-royi yana zaune a Negeb.

63. A gabatowar maraice, sai Ishaku ya fita saura ya yi tunani, ya ɗaga idanunsa ya duba, ya ga raƙuma suna zuwa.

64. Da Rifkatu ta ɗaga idanunta, ta hangi Ishaku, sai ta sauka daga raƙumi,

65. ta ce wa baran, “Wane ne mutumin can da yake zuwa daga saura garin ya tarye mu?”Sai baran ya ce, “Ai, maigidana ne.” Ta ɗauki mayafinta ta yi lulluɓi.

66. Sai baran ya faɗa wa Ishaku dukan abin da ya yi.

67. Ishaku kuwa ya shiga da ita cikin alfarwarsa ya ɗauki Rifkatu ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta. Ta haka Ishaku ya ta'azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

Karanta cikakken babi Far 24