Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 24:52-62 Littafi Mai Tsarki (HAU)

52. Sa'ad da baran Ibrahim ya ji wannan, ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya yi sujada a gaban Ubangiji.

53. Sai baran ya kawo kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, ya bai wa Rifkatu, ya kuma ba ɗan'uwanta da mahaifiyarta kayan ado masu tsada.

54. Shi da mutanen da suke tare da shi suka ci suka sha, suka kwana wurin. Da suka tashi da safe, sai ya ce, “A sallame ni, in koma wurin maigidana.”

55. Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Ka bar budurwar tare da mu har ɗan lokaci, kada ya gaza kwana goma, bayan wannan ta tafi.”

56. Amma ya ce musu, “Kada ku makarar da ni, tun da yake Allah ya arzuta tafiyata, a sallame ni domin in koma wurin maigidana.”

57. Suka ce, “Za mu kira budurwar mu tambaye ta.”

58. Suka kirawo Rifkatu suka ce mata, “Za ki tafi tare da wannan mutum?”Sai ta ce, “Zan tafi.”

59. Suka kuwa sallami Rifkatu 'yar'uwarsu da uwar goyonta, da baran Ibrahim da mutanensa.

60. Suka sa wa Rifkatu albarka, suka ce mata,“'Yar'uwarmu, ki zama mahaifiyardubbai,Har dubbai goma,Bari zuriyarki kuma su gāji ƙofofinmaƙiyansu!”

61. Sai Rifkatu da kuyanginta suka tashi suka hau raƙuman, suka bi mutumin. Haka nan kuwa baran ya ɗauki Rifkatu ya koma.

62. A lokacin kuwa Ishaku ya riga ya zo daga Biyer-lahai-royi yana zaune a Negeb.

Karanta cikakken babi Far 24