1. Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya,
2. sa an nan ta rasu a Kiriyat-arba, wato Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makoki, yana baƙin ciki domin Saratu.
3. Ibrahim ya bar gawar matarsa, ya je ya ce wa Hittiyawa,
4. “Ni baƙo ne, ina tsakaninku, ina zaman baƙunci. Ku sayar mini da wurin yin makabarta, domin in binne matata, in daina ganinta!”