Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 2:22-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. haƙarƙarin nan kuwa da Ubangiji Allah ya cire daga mutumin ya yi mace da shi, ya kuwa kawo ta ga mutumin.

23. Sai mutumin ya ce, “Yanzu dai wannan ƙashi ne daga ƙasusuwana, nama ne kuwa daga namana, za a kira ta mace, don daga cikin mutum aka ciro ta.”

24. Domin haka mutum yakan rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya kuwa manne wa matarsa, sun zama ɗaya.

25. Da mutumin da matarsa dukansu biyu a tsiraice suke, ba su kuwa ji kunya ba.

Karanta cikakken babi Far 2