Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 19:3-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka ratse suka shiga gidansa, ya shirya musu liyafa, ya toya musu abinci marar yisti, suka ci.

4. Amma kafin su shiga barci, mutanen birnin Saduma, samari da tsofaffi, dukan mutane gaba ɗaya suka kewaye gidan.

5. Suka kira Lutu suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka da daren nan? Fito mana da su waje, don mu yi luɗu da su.”

6. Lutu ya fita daga cikin gida ya rufe ƙofar a bayansa ya je wurin mutane,

7. ya ce, “Ina roƙonku 'yan'uwana, kada ku aikata mugunta haka.

Karanta cikakken babi Far 19