Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 18:27-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji, ni da nake ba kome ba ne, amma turɓaya ne da toka.

28. Da a ce za a rasa biyar daga cikin adalai hamsin ɗin, za ka hallaka birnin duka saboda rashin biyar ɗin?”Sai ya ce, “Ba zan hallaka shi ba in na sami arba'in da biyar a wurin.”

29. Ya kuma sāke yin masa magana, ya ce, “Da a ce za a sami arba'in a wurin fa?”Ya amsa ya ce, “Sabili da arba'in ɗin ba zan yi ba.”

30. Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan yi magana. Da a ce za a sami talatin a wurin fa?”Ya amsa, “Ba zan yi ba, in na sami talatin a wurin.”

31. Ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji. Da a ce za a sami ashirin a wurin fa?”Ya amsa ya ce, “Sabili da ashirin ɗin ba zan hallaka shi ba.”

32. Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan sāke yin magana, sau ɗayan nan kaɗai. Da a ce za a sami goma a wurin fa?”Ya amsa ya ce, “Sabili da goma ɗin ba zan hallaka shi ba.”

33. Ubangiji kuwa ya yi tafiyarsa, bayan ya gama magana da Ibrahim. Ibrahim kuwa ya koma gida.

Karanta cikakken babi Far 18