Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ezra 6:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincike ɗakin littattafai na Babila, inda aka ajiye takardun shaida.

2. Sai aka sami takarda a Ekbatana, babban lardin Mediya. A cikin takardar aka iske rubutu don tunawa.

3. “A shekara ta fari ta sarautar sarki Sairus, sai ya ba da izini a sāke gina Haikalin Allah da yake a Urushalima, wurin da za a miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Sai a aza harsashi da ƙarfi. Tsayinsa zai zama kamu sittin, fāɗinsa kuwa kamu sittin.

4. Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako, a kuma biya kuɗin aikin daga baitulmalin sarki.

5. A kuma kawo kwanonin nan na zinariya da na azurfa cikin Haikalin Allah, waɗanda Nebukadnezzar ya kwaso daga cikin Haikali a Urushalima ya kawo Babila, a komar da su, a mayar da su a Haikali a Urushalima, a ajiye kowanne a wurinsa a Haikalin Allah.”

6. Sarki Dariyus ya ce, “Zuwa ga Tattenai, mai mulkin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu, wato ma'aikatan hukuma na lardin Yammacin Kogi, ku nisance su.

Karanta cikakken babi Ezra 6