Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 8:14-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Sai ya kai ni a bakin ƙofar arewa ta Haikalin Ubangiji, ga kuwa mata a zaune suna kuka domin gunkin nan, Tammuz.

15. Sa'an nan ya ce mini, “Ya ɗan mutum, ka ga wannan? Har yanzu ma za ka ga abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”

16. Ya kuma kai ni farfajiya ta can cikin Haikalin Ubangiji. Na ga mutum wajen ashirin da biyar a ƙofar Haikalin Ubangiji a tsakanin shirayi da bagade, suka juya wa Haikalin Ubangiji baya, suka fuskanci wajen gabas, suna yi wa rana sujada.

17. Ya kuma ce mini, “Ya ɗan mutum, ka ga wannan? Wato mutanen Yahuza ba su mai da aikata abubuwa masu banƙyama nan wani abu ba. Sun cika ƙasar da hargitsi, suna ta tsokanar fushina. Ga shi, suna hura hanci a gabana.(Eze 9.9; Eze 16.26

18. Zan yi hukunci mai zafi, ba zan yafe ba, ba kuma zan ji tausayi ba, ko da yake suna kuka da babbar murya a kunnuwana ba zan ji su ba.”

Karanta cikakken babi Ez 8