Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 34:19-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake da ƙafafunku, su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku!’

20. “Saboda haka, ni, Ubangiji Allah, na ce, ‘Zan shara'anta tsakanin turkakkun tumaki da ramammu.

21. Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku, har kun watsar da su.

22. Zan ceci garken tumakina, ba za su ƙara zama ganima ba. Zan kuma shara'anta tsakanin tunkiya da tunkiya.

23. Zan sa musu makiyayi guda, wato bawana Dawuda. Zai yi kiwonsu, ya zama makiyayinsu.

24. Ni kuma, Ubangiji, zan zama Allahnsu. Bawana Dawuda kuwa zai zama sarkinsu.’ Ni Ubangiji na faɗa.

Karanta cikakken babi Ez 34