Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 32:6-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Zan watsar da jininka a ƙasa da tuddai,Magudanan ruwa za su cika da jininka.

7. Sa'ad da na shafe ka, zan rufe sammai,In sa taurarinsu su duhunta,Zan sa girgije ya rufe rana,Wata kuma ba zai haskaka ba.

8. Dukan haskokin sama zan sa su zama duhu a gare ka,In sa ƙasarka ta duhunta, ni Ubangiji Allah na faɗa.’

9. “Zukatan al'ummai da yawa za su ɓaci, sa'ad da na baza labarin halakarka a ƙasashen da ba ka sani ba.

Karanta cikakken babi Ez 32