Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 31:2-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Ɗan mutum, ka ce wa Fir'auna, Sarkin Masar, da jama'arsa.‘Da wa za a kamanta girmanka?

3. Kana kama da Assuriya mai kama da itacen al'ul a Lebanon,Mai rassa masu kyau da inuwar kurmi,Mai tsayi ainun, kansa ya kai cikin gizagizai.

4. Ruwa ya sa ya yi girma,Danshi ya sa ya yi tsayi.Koguna sun gudu kewaye da wurin da aka shuka shi.Yana aikar da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.

5. Sai ya yi tsayi fiye da dukan itatuwan da suke a kurmi,Rassansa suka yi kauri, suka kuma yi tsayi,Saboda isasshen ruwa a lokacin tohonsa.

6. Dukan tsuntsayen sararin sama sun yi sheƙunansu a rassansa,Namomin jeji kuma suka haifi 'ya'yansu ƙarƙashin rassansa.Dukan al'ummai suka zauna ƙarƙashin inuwarsa.

7. Girmansa yana da kyau, haka kuma dogayen rassansa,Gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin ruwa.

8. Ko itatuwan al'ul da suke cikin gonar Allah, ba su kai kyansa ba.Itatuwan kasharina kuma ba su kai rassansa ba.Itatuwan durumi kuma ba su kai rassansa ba.Ba wani itace a gonar Allah wanda ya kai kyansa.

9. Na sa shi ya yi kyau, ga kuma rassansa da yawa.Dukan itatuwan Aidan, waɗanda suke cikin gonar Allah sun yi ta jin ƙyashinsa.’

10. Domin haka Ubangiji Allah ya ce, “Saboda ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, zuciyarsa kuwa ta yi fariya saboda tsayinsa,

Karanta cikakken babi Ez 31