Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 31:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A kan rana ta fari ga watan uku a shekara ta goma sha ɗaya, Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce,

2. “Ɗan mutum, ka ce wa Fir'auna, Sarkin Masar, da jama'arsa.‘Da wa za a kamanta girmanka?

3. Kana kama da Assuriya mai kama da itacen al'ul a Lebanon,Mai rassa masu kyau da inuwar kurmi,Mai tsayi ainun, kansa ya kai cikin gizagizai.

4. Ruwa ya sa ya yi girma,Danshi ya sa ya yi tsayi.Koguna sun gudu kewaye da wurin da aka shuka shi.Yana aikar da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.

5. Sai ya yi tsayi fiye da dukan itatuwan da suke a kurmi,Rassansa suka yi kauri, suka kuma yi tsayi,Saboda isasshen ruwa a lokacin tohonsa.

Karanta cikakken babi Ez 31