Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 25:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. domin haka zan miƙa hannuna gāba da ku, zan bashe ku, ku lalace a ƙasashe, zan hallaka ku. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji.”

8. Ubangiji Allah ya ce, “Da yake Mowab da Seyir sun ce mutanen Yahuza sun zama kamar al'ummai,

9. saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab daga garuruwan da suke kan iyaka, waɗanda su ne darajarta, wato Bet-yeshimot, da Ba'al-meyon, da Kiriyatayim.

10. Zan bashe ta duk da Ammonawa su zama abin mallakar mutanen gabas, don kada um'ƙara tunawa da su a cikin al'ummai.

11. Zan hukunta Mowab, sa'an nan za ta sani ni ne Ubangiji.”

Karanta cikakken babi Ez 25