9. “Saboda haka, ni Ubangiji Allah na ce,‘Kaitonka, ya birni, mai zubar da jini!Ni kuma zan tsiba itace da yawa.
10. Ka tula gumagumai, ka kunna wuta,Ka tafasa naman sosai,Ka zuba kayan yaji a ciki,Ka bar ƙasusuwan su ƙone.
11. Ka ɗora tukunyar da ba kome cikinta a bisa garwashiDomin ta yi zafi, tagullarta ta yi ja wur,Domin dauɗarta ta narke a ciki,Tsatsarta kuma ta ƙone.
12. Ta gajiyar da ni a banza,Wutar ba ta fitar da yawan tsatsarta ba.