Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Laifofin Urushalima

1. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

2. “Kai ɗan mutum, za ka shara'anta? Za ka shara'anta birni mai kisankai? To, sai ka faɗa masa dukan ayyukansa na banƙyama.

3. Sai ka ce masa, ‘Ni Ubangiji Allah na ce, birnin da yake kisankai, yana kuma bauta wa gumaka don ya ƙazantar da kansa, lokacinsa zai yi!

4. Ka yi laifi saboda ka zubar da jini, ka ƙazantar da kanka da gumakan da ka yi. Saboda haka ka matso da lokacinka kusa, ƙayyadaddun shekarunka sun cika. Domin haka na maishe ka abin zargi ga sauran al'umma, da abin ba'a ga dukan ƙasashe.

5. Waɗanda suke kusa, da waɗanda suke nesa za su yi maka ba'a, gama kai shahararren mugu ne, cike da hargitsi.

6. Ga shi, kowane shugaban Isra'ila da yake cikinka ya himmantu ga zub da jini bisa ga ikonsa.

7. A cikinka ana raina mahaifi da mahaifiya, ana kuma tsananta wa baƙo, ana cin zalin marayu, da gwauruwa, wato wadda mijinta ya mutu.

8. Ka raina tsarkakan abubuwa, ka kuma ɓata ranar Asabar ɗina.

9. Akwai mutane a cikinka waɗanda suke haddasa rikici don su zubar da jini, akwai kuma mutanen da suke cin abinci a matsafai, akwai mutanen da suke aikata lalata.

10. A cikinka, mutane suna kwana da matan mahaifansu, waɗansu suna kwana da mata a lokacin hailarsu.

11. Wani yakan yi lalata da matar maƙwabcinsa, wani kuma ya kwana da matar ɗansa, wani ya kwana da 'yar'uwarsa, wato 'yar mahaifinsa.

12. A cikinka mutane suka karɓi toshi don su zub da jini. Kana ba da rance da ruwa da ƙari, kana kuma cin riba a kan maƙwabcinka saboda cutar da kake yi masa, ka kuwa manta da ni, ni Ubangiji na faɗa.

13. “‘Ga shi, na tafa hannuna saboda ƙazamar riba da ka ci, da jinin da ka zubar.

14. Zuciyarka za ta iya ɗaurewa, hannuwanka kuma za su ƙarfafa a ranar da zan gamu da kai? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.

15. Zan watsar da kai cikin al'ummai, in warwatsa ka cikin ƙasashe, zan kawo ƙarshen mugayen ayyukanka.

16. Za a ƙasƙantar da kai a gaban sauran al'umma, sa'an nan za ka sani ni ne Ubangiji.”’

Tanderun Tsarkakewa

17. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

18. “Ɗan mutum, mutanen Isra'ila sun zama kamar ƙwan maƙera a gare ni. Dukansu sun zama kamar tagulla, da kuza, da baƙin ƙarfe, da darma, a tanderu, sun zama ƙwan maƙera na azurfa.

19. Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce da yake dukanku kun zama ƙwan maƙera zan tattara dukanku a Urushalima.

20. Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da darma, da kuza a cikin tanderu, su hura wuta a kansu, don su narkar da su, haka zan tattara ku da zafin fushina in narkar da ku.

21. Zan tattaro ku, in hura muku wutar hasalata, za ku narke a cikinta.

22. Kamar yadda azurfa takan narke a cikin tanderu, haka kuma za ku narke, za ku sani ni, Ubangiji ne, na zubo muku da zafin fushina.”

Laifofin Shugabannin Isra'ila

23. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

24. “Ɗan mutum, ka ce mata, ‘Ke ƙasa ce marar tsarki, wadda ba a yi ruwan sama a kanki ba a lokacin da na yi fushi.’

25. Annabawanta suna kama da zakoki masu ruri waɗanda suke yayyage ganimar da suka samu. Sun kashe mutane, sun ƙwace dukiya da abubuwa masu daraja. Sun sa mata da yawa sun rasa mazansu.

26. Firistocinta sun karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana. Ba su bambanta tsakanin abin da yake mai tsarki da marar tsarki ba, ba su kuma koyar da bambancin da yake tsakanin halal da haram ba. Ba su kiyaye ranar Asabar ɗina ba, da haka suke saɓon sunana.

27. Shugabanninta sun zama kamar kyarketai masu yayyage ganima. Suna yin kisankai don su sami ƙazamar riba.

28. Annabawanta sun yi musu shafe da farar ƙasa, wato wahayan da suke gani, da duban da suke yi musu ƙarya ne. Suna cewa Ubangiji ne ya faɗa, alhali kuwa ni Ubangiji ban faɗa musu kome ba.

29. Mutanen ƙasar sun yi zalunci, sun yi fashi, sun zalunci matalauta da masu fatara. Ba su yi wa baƙo adalci ba, sai cuta.

30. Sai na nemi mutum a cikinsu wanda zai gina garun ya tsaya a hauren garun a gabana, domin kada in hallaka ƙasar, amma ban sami kowa ba.

31. Saboda haka na kwarara musu fushina, na ƙone su da wutar hasalata, na ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”