Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 21:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Idan sun tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Saboda labarin abin da yake zuwa. Sa'ad da ya zo, kowace zuciya za ta narke, hannuwa duka za su yi suwu, kowane ruhu kuma zai suma, gwiwoyi duka kuwa za su rasa ƙarfi kamar ruwa. Ga shi, abin yana zuwa, zai tabbata,’ ni Ubangiji Allah na faɗa.”

8. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

9. “Ya ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce ni Ubangiji na ce,‘Takobi, takobi wasasshe,Kuma gogagge!

10. An wasa shi domin kisa,An goge shi don ya yi walwal kamar walƙiya!’Ba wanda zai iya tsai da shi, domin kun ƙi karɓar shawara.

11. An ba da takobin a goge shi domin a riƙe. An wasa shi, an kuma goge shi domin a ba mai kashewa.

Karanta cikakken babi Ez 21