Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 16:23-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. “Bayan dukan muguntarki (Kaito, kaitonki! Ni Ubangiji Allah na faɗa),

24. sai kika gina wa kanki ɗakunan tsafi a kowane fili.

25. Kika kuma gina ɗakin tsafi a kowane titi. Kin waƙala darajarki, kin ba da kanki ga kowane mai wucewa, ta haka kika yawaita karuwancinki.

26. Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi. Kin yawaita karuwancinki don ki tsokani fushina.

27. “Domin haka na miƙa hannuna gāba da ke, na rage rabonki, na ba da ke ga abokin gābanki masu haɗama, 'yan matan Filistiyawa waɗanda suka ji kunya saboda halinki na lalata.

Karanta cikakken babi Ez 16