Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 8:15-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Sa'ad da ni Daniyel, na ga wahayin, ina so in gane, sai ga wani kamar mutum ya tsaya a gabana.

16. Na kuma ji muryar mutum a gāɓar Ulai ta ce, “Jibra'ilu, ka sa wannan mutum ya gane wahayin.”

17. Don haka sai ya zo kusa da inda nake tsaye. Da ya zo sai na firgita, na faɗi rubda ciki.Amma ya ce mini, “Ɗan mutum, wannan wahayi yana a kan lokaci na ƙarshe ne.”

18. Sa'ad da yake magana da ni, sai barci mai nauyi ya kwashe ni da nake kwance rubda ciki, amma sai ya taɓa ni, ya tashe ni tsaye.

Karanta cikakken babi Dan 8