Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Dan 6:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Sai aka kawo dutse aka rufe bakin kogon, sarki kuwa ya hatimce shi da hatiminsa, da hatimin fādawansa, don kada a sāke kome game da Daniyel.

18. Sarki ya koma fādarsa, ya kwana yana azumi, bai ci abinci ba, ya kuma kāsa yin barci.

19. Gari na wayewa, sai sarki ya tashi, ya tafi da gaggawa wurin kogon zakoki.

20. Da ya zo kusa da kogon da Daniyel yake, sai ya ta da murya ya yi kira da damuwa, ya ce wa Daniyel, “Ya Daniyel, bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta masa kullum, yana da ikon cetonka daga zakoki?”

21. Sai Daniyel ya ce wa sarki, “Ran sarki ya daɗe!

Karanta cikakken babi Dan 6