Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 9:20-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni,A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne.Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi.

21. Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa.Na gaji da rayuwa.

22. Don haka ban damu da kome ba.Da marar laifin da mai laifin duk, Allah zai hallaka mu.

23. Sa'ad da marar laifi ya mutu farat ɗaya,Allah yakan yi dariya.

24. Allah ya ba da duniya ga mugaye,Ya makantar da dukan alƙalai,Idan ba Allah ne ya yi haka nan ba, to, wa ya yi?

25. “Kwanakina suna shuɗewa da sauri, ba mai kyau ko ɗaya.

Karanta cikakken babi Ayu 9