Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 9:13-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. “Allah ba zai huce fushinsa ba.Ya murƙushe maƙiyansa waɗanda suka taimaki dodon ruwan nan da ake kira Rahab, wanda ya tayar masa.

14. To, ƙaƙa zan yi in samo kalmomin da zan amsa wa Allah?

15. Ko da yake ba ni da laifi,Duk da haka iyakar abin da zan iya yi ke nan,In roƙi Allah ya yi mini jinƙai,Shi da yake alƙalina.

16. Amma duk da haka ko ya yardar mini in yi magana ma,Ban yi tsammani zai saurare ni ba.

17. Shi ya aiko da hadura, suka yi kacakaca da ni,Suka ƙuƙƙuje ni, ga shi kuwa, ba wani dalilin da ya sa ya yi mini rauni.

18. Ya hana ni in ko shaƙata,Ina jin haushin dukan abin da yake yi mini.

19. In gwada ƙarfi ne?To, a iya gwada wa Allah ƙarfi?In kai shi ƙara ne?Wa zai sa shi ya je?

20. Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni,A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne.Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi.

21. Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa.Na gaji da rayuwa.

Karanta cikakken babi Ayu 9