Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 9:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ayuba ya amsa.

2. “Ai, na taɓa jin waɗannan duka,Amma ta ƙaƙa mutum zai yi jayayya da Allah har ya yi nasara?

3. Ta ƙaƙa za ka iya jayayya da shi?Yana yiwuwa ya yi maka tambayoyi guda dubuWaɗanda ba wanda zai iya ba da amsarsu.

4. Allah mai hikima ne, mai iko,Ba wanda zai iya ja in ja da shi.

5. Yakan kawar da manyan duwatsu farat ɗaya,Ya hallaka su da fushinsa,

6. Allah yakan aiko da girgizar ƙasa, ya girgiza duniya,Yakan jijjiga ginshiƙan da duniya take zaune a kansu.

Karanta cikakken babi Ayu 9