Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 8:2-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Ka gama maganganunka marasa kan gado duka?

3. Allah bai taɓa yin danniya ba,Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba.

4. Lalle 'ya'yanka sun yi wa Allah zunubi,Don haka ya hukunta su yadda ya cancanta.

5. Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki.

6. Idan kana da tsarki da aminci, Allah zai taimake ka,Ya maido da iyalin gidanka, ya yi maka sakayya.

7. Duk hasarar dukiyan nan da ka yi, ba kome ba neIn aka gwada da abin da Allah zai ba ka nan gaba.

8. “Ka tsai da zuciyarka a kan hikima irin ta zamanin dā.Ka kuma yi ta yin tunani a kan gaskiyar da kakanninmu suka koya.

9. Kwanakinmu 'yan kaɗan ne kawai,Ba mu san kome ba,Mu inuwa ne kawai a fuskar duniya.

Karanta cikakken babi Ayu 8