Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 40:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Ayuba ya amsa wa Ubangiji ya ce,

4. “Ai, ni ba a bakin kome nake ba,Wace amsa zan ba ka?Na rufe bakina na yi gam.

5. Ai, na riga na yi magana sau ɗaya, har ma sau biyu,Ba zan amsa ba, ba zan ƙara cewa kome ba.”

6. Sa'an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba daga cikin guguwa, ya ce,

7. “Tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji,Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.

8. Kai kanka za ka sa mini laifi?Za ka kā da ni don kai ka barata?

Karanta cikakken babi Ayu 40