Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 4:6-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Kana yi wa Allah sujada,Ba wani laifi a zamanka,Ya kamata ka amince ka sa zuciya.

7. “Yanzu fa sai ka yi tunani.Ka faɗi bala'i ɗaya wanda ya taɓa fāɗa wa adalin mutum.

8. Na taɓa ganin mutane suna huɗe gonar mugunta,Suna shuka mugunta,Suka kuwa girbe mugunta.

9. A cikin fushinsa Allah yakan hallaka su kamar hadiri.

10. Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki,Amma Allah yakan sa su yi tsit,Ya kakkarya haƙoransu.

11. Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci,Haka nan za su mutu, 'ya'yansu kuwa su warwatse duka.

12. “Wata rana wani saƙo ya zo a hankali,Har da ƙyar nake iya ji,

13. Kamar wani irin mafarki mai razanarwa yake,Wanda ya hana ni jin daɗin barcina.

14. Na yi rawar jiki ina makyarkyata,Duk jikina yana ta ɓare-ɓare don tsoro.

15. Wata iska marar ƙarfi ta taɓa fuskata,Sai fatar jikina ta yanƙwane saboda fargaba.

16. Na ga wani abu can yana tsaye,Na zura ido, amma ban san kowane irin abu ba ne,Ina cikin wannan hali sai na ji murya,

Karanta cikakken babi Ayu 4