Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 38:7-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sa'ad da taurarin asuba suka raira waƙa tare,Sai mala'iku duka suka yi sowa saboda murna.

8. “Wa ya yi wa teku iyakaSa'ad da ta tumbatso daga zurfafa?

9. Sa'ad da na suturta ta da gizagizai,Na yi mata maɗauri da duhu ƙirin.

10. Na sa mata iyakoki,Na sa mata ƙyamare da ƙofofi,

11. Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan,Ba za ki wuce ba.Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’

12. “Ayuba, a dukan kwanakinkaKa taɓa umartar wayewar gari,Ko ka sa alfijir ya keto?

13. Da gari ya waye,Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?

14. Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi,Yakan rine kamar riga.

15. Akan hana wa mugaye haske,Sa'ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su.

16. “Ko ka taɓa shiga cikin maɓuɓɓugan teku?Ka taɓa yin tafiya a cikin zurfin lallokin teku?

17. An taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa?Ko kuwa ka taɓa ganin ƙofofin duhu ƙirin?

Karanta cikakken babi Ayu 38