Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 38:11-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan,Ba za ki wuce ba.Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’

12. “Ayuba, a dukan kwanakinkaKa taɓa umartar wayewar gari,Ko ka sa alfijir ya keto?

13. Da gari ya waye,Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?

14. Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi,Yakan rine kamar riga.

15. Akan hana wa mugaye haske,Sa'ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su.

16. “Ko ka taɓa shiga cikin maɓuɓɓugan teku?Ka taɓa yin tafiya a cikin zurfin lallokin teku?

17. An taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa?Ko kuwa ka taɓa ganin ƙofofin duhu ƙirin?

18. Ko ka san iyakar fāɗin duniya?Ka amsa mini in ka san dukan waɗannan.

19. “Ina hanya zuwa wurin da haske yake?A ina kuma duhu yake?

20. Ka san iyakarsa ko mafarinsa?

Karanta cikakken babi Ayu 38