1. Ubangiji ya yi magana da Ayuba ta cikin guguwa.
2. “Wane ne wannan da yake ɓāta shawaraDa maganganu marasa ma'ana?
3. Ka tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji,Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa.
4. A ina kake sa'ad da na aza harsashin gina duniya?Faɗa mini idan ka sani.