Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 36:5-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. “Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa,Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira.

6. Ba ya rayar da masu laifi,Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu.

7. Yakan kiyaye waɗanda suke aikata gaskiya,Yakan kafa su har abada tare da sarakuna,A gadon sarauta, ya ɗaukaka su.

8. Amma idan aka ɗaure su da sarƙoƙi,Da kuma igiyar wahala,

9. Sa'an nan yakan sanar da su aikinsuDa laifofin da suke yi na ganganci.

10. Yakan sa su saurari koyarwa,Da umarnai, cewa su juya, su bar mugunta.

11. Idan suka kasa kunne suka bauta masa,Za su cika kwanakinsu da wadata,Shekarunsu kuma da jin daɗi.

12. Amma idan ba su kasa kunne ba,Za a hallaka su da takobi,Su mutu jahilai.

13. “Waɗanda ba su da tsoron Allah a zuciyarsu,Suna tanada wa kansu fushi,Ba su neman taimako sa'ad da ya ɗaure su.

Karanta cikakken babi Ayu 36