Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 35:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Amma ba su juyo wurin Allah Mahaliccinsu ba,Wanda yakan sa a raira waƙa da dare,

11. Wanda yake koya mana fiye da namomin jeji da suke a duniya,Wanda ya sa muka fi tsuntsayen sama hikima.

12. Suka yi kira don taimako, amma Allah bai amsa ba,Saboda suna da girmankan mugaye.

13. Hakika Allah bai ji holoƙon kukansu ba,Allah Mai Iko Dukka kuwa bai kula da shi ba.

14. “Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba?Da kake cewa ƙararka tana gabansa,Jiransa kake yi?

Karanta cikakken babi Ayu 35