Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 34:31-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. “Akwai wanda zai ce wa Allah, ‘Ni horarre ne,Ba zan ƙara yin laifi ba?

32. Ka koya mini abin da ban sani ba,Idan na yi laifi, ba zan ƙara yi ba.’

33. Zai kuɓutar domin ya gamshe ka saboda ka ƙi yarda?Tilas kai za ka zaɓa, ba ni ba,Saboda haka sai ka hurta abin da ka sani.

34. “Haziƙan mutane da mutum mai hikima da suka ji ni za su ce,

35. ‘Ayuba yakan yi magana ne ba tare da sanin abin da yake yi ba,Maganarsa ba ta mai hangen nesa ba ce.

36. Da ma a gwada Ayuba har ƙarshe,Saboda amsar da yake bayarwa ta mugaye.

37. Gama ya ƙara zunubinsa da tayarwa,Yana tafa hannunsa a tsakaninmu,Yana yawaita maganganunsa gāba da Allah.’ ”

Karanta cikakken babi Ayu 34