Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 33:29-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,

30. Don ya komo da ran mutum daga kabari,Domin a haskaka shi da hasken rai.

31. “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne,Ga abin da nake faɗa,Ka yi shiru, zan yi magana.

32. Amma idan kana da ta cewa, to, amsa,Yi magana, gama ina so in kuɓutar da kai.

33. In kuwa ba haka ba, sai ka yi shiru,Ka kasa kunne gare ni,Zan kuwa koya maka hikima.”

Karanta cikakken babi Ayu 33