Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 33:28-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari,Raina kuwa zai ga haske.’

29. “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,

30. Don ya komo da ran mutum daga kabari,Domin a haskaka shi da hasken rai.

31. “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne,Ga abin da nake faɗa,Ka yi shiru, zan yi magana.

Karanta cikakken babi Ayu 33