18. Yakan hana su zuwa kabari,Ya hana ransu halaka da takobi.
19. “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa,Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa,
20. Ransa yana ƙyamar abinci,Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa.
21. Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje.
22. Yana gab da shiga kabari,Ransa yana hannun mala'ikun mutuwa.
23. “Da a ce akwai wani mala'ika mai sulhuntawa a tsakani,Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum,