1. “Amma yanzu, kai Ayuba, ka yarda ka ji maganata,Ka kasa kunne ga dukan abin da zan faɗa.
2. Ga shi, na buɗe baki in yi magana.
3. Maganar da zan hurta ainihin gaskiyar da take a zuciyata ce,Abin da zan faɗa kuma dahir ne.
4. Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai.