Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 32:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Na ce wa kaina, ‘Ya kamata kwanaki su yi magana,Yawan shekaru kuma su koyar da hikima.’

8. Amma Ruhun Allah Mai Iko Dukka ne wanda yake cikin mutum,Yakan ba mutane basira.

9. Ba tsofaffi ne masu wayo ba,Ba kuma masu yawan shekaru kaɗai yake gane abin da yake daidai ba.

10. Don haka na ce ku kasa kunne gare ni,Bari in faɗa muku nawa ra'ayi.

11. “Ga shi, na dakata na ji maganarku,Na kasa kunne ga maganarku ta hikima,Tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa.

Karanta cikakken babi Ayu 32