Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 31:11-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai,Wanda alƙalai ne za su hukunta.

12. Za ta zama wuta mai ci har ta hallaka,Za ta cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.

13. “Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba,Sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina,

14. To, wace amsa zan ba Allah sa'ad da ya tashi don ya hukuntar?Me zan iya faɗa sa'ad da Allah ya zo yi mini shari'a?

15. Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa,Ba shi ne ya halicce su ba?Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa?

16. “Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba,Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba,

17. Ko kuwa in bar marayu da yunwa sa'ad da nake cin abincina,

18. Tun suna yara nake goyonsu,Ina lura da su kamar 'ya'yan cikina.

Karanta cikakken babi Ayu 31