Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 30:5-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Aka kore su daga cikin mutane,Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo,

6. Sai a kwazazzabai suke zamaDa a ramummuka da kogwannin duwatsu.

7. Suka yi ta kuka a jeji,Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.

8. Mutane ne marasa hankali marasa suna!Aka kore su daga ƙasar.

9. “Yanzu na zama abin waƙa gare su,Abin ba'a kuma a gare su.

10. Suna ƙyamata, guduna suke yi,Da ganina, sai su tofa mini yau.

11. Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,Saboda haka sun raba ni da zuriyata,

12. A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini,Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.

Karanta cikakken babi Ayu 30