Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 3:1-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ayuba ya yi magana ya la'anci ranar da aka haife shi.

2. Ya ce,“Ya Ubangiji, ka la'anci ranan nan da aka haife ni.

3. Ka la'anci daren nan da aka yi cikina.

4. Ka mai da ranan nan ta zama duhu, ya Allah.Kada a ƙara tunawa da wannan rana,Kada haske ya ƙara haskakata.

5. Ka sa ta zama ranar duhu baƙi ƙirin.Ka rufe ta da gizagizai, kada hasken rana ya haskaka ta.

6. Ka shafe wannan dare daga cikin shekara,Kada kuma a ƙara lasafta shi.

7. Ka sa daren ya zama marar amfani, daren baƙin ciki.

8. Ka faɗa wa masu sihiri su la'anci wannan rana,Su waɗanda suke umartar dodon ruwa.

9. Ka hana gamzaki haskakawa,Kada ka bar daren nan ya sa zuciya ga wayewar gari,

10. Ka la'anci daren nan da aka haife ni,Da ya jefa ni a baƙin ciki da wahala.

11. “Da ma na mutu tun a cikin cikin uwata,Ko kuwa da haihuwata in mutu.

Karanta cikakken babi Ayu 3