Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 26:2-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. “Kai ne mai taimakon marar ƙarfi,Kai ne mai ceton rarrauna!

3. Kai ne kake ba marar hikima shawara,Kai kake sanar da ilimi mai ma'ana a wadace!

4. Kana tsammani wane ne zai ji maganganunka duka?Wane ne ya iza ka ka yi irin wannan magana?

5. “Lahira tana rawa,Mazaunanta suna rawar jiki don tsoro.

6. Lahira tsirara take a gaban Allah,Haka kuma Halaka take a gaban Allah.

7. Allah ne ya shimfiɗa arewa a sarari kurum,Ya rataya duniya ba bisa kan kome ba.

8. Allah ne ya cika gizagizai masu duhu da ruwa,Girgijen kuwa bai kece ba.

9. Ya rufe kursiyinsa, ya shimfiɗa girgije a kansa.

10. Ya shata da'ira a kan fuskar teku,A kan iyakar da take tsakanin haske da duhu.

11. Ginshiƙan samaniya sun girgiza,Sun firgita saboda tsautawarsa.

12. Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku,Da saninsa ya hallaka dodon ruwan nan, wato Rahab.

Karanta cikakken babi Ayu 26