Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 21:7-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Me ya sa Allah yake barin mugayeHar su tsufa su kuma yi arziki?

8. 'Ya'yansu da jikokinsu sukan girma a idonsu.

9. Allah bai taɓa aukar wa gidajensu da bala'i ba,Ba su taɓa zama a razane ba.

10. Hakika shanunsu suna ta hayayyafa,Suna haihuwa ba wahala.

11. 'Ya'yansu suna guje-guje,Suna tsalle kamar 'yan raguna,

12. Suna rawa ana kaɗa garaya,Ana busa sarewa.

13. Suka yi zamansu da salama,Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba.

14. Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum,Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.

15. Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah,Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida.

16. Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara,Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.

17. “An taɓa kashe hasken mugun mutum?Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu?Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi,

18. Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa?Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa?

19. “Kukan ce Allah yakan hukunta yaro saboda zunuban mahaifinsa.A'a! Allah dai yakan hukunta wa masu zunubi.Ya kuma nuna ya yi haka saboda zunubansu ne.

20. Bari dai a hukunta masu zunubiSu kuma ga hasalar Allah.

Karanta cikakken babi Ayu 21