30. A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci,A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.
31. Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun,Ko ya mayar masa da martani.
32. Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi,A inda ake tsaron kabarinsa,
33. Dubban mutane sukan tafi wurin jana'izarsa,Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali.
34. “Amma ku, ƙoƙari kuke yi ku ta'azantar da ni da maganganun banza.Duk abinda kuka faɗa ƙarya ne!”