Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 21:25-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Waɗansu kuwa ba su taɓa sanin farin ciki ba.Sukan yi dukan kwanakinsu su mutu da baƙin ciki.

26. Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne,Tsutsotsi su lulluɓe su duka.

27. “Na san irin tunaninku na hassada,

28. Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu,Wato mutumin da yake aikata mugunta?’

29. “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba?Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?

30. A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci,A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.

31. Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun,Ko ya mayar masa da martani.

32. Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi,A inda ake tsaron kabarinsa,

Karanta cikakken babi Ayu 21