Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 21:20-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Bari dai a hukunta masu zunubiSu kuma ga hasalar Allah.

21. Bayan rasuwar mutum,Ruwansa ne ya sani ko 'ya'yansa suna jin daɗi?

22. Mutum zai iya koya wa Allah?Mutum zai iya shara'anta wa Allah Mai Iko Dukka?

23. “Waɗansu mutane sukan yi zamansu ba ciwon kome har ranar mutuwarsu,Suna cikin farin ciki da jin daɗi,

24. Jikunansu kuwa sun yi ɓulɓul.

25. Waɗansu kuwa ba su taɓa sanin farin ciki ba.Sukan yi dukan kwanakinsu su mutu da baƙin ciki.

26. Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne,Tsutsotsi su lulluɓe su duka.

27. “Na san irin tunaninku na hassada,

28. Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu,Wato mutumin da yake aikata mugunta?’

29. “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba?Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba?

30. A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci,A kullum mugun ne kaɗai yakan kuɓuta.

Karanta cikakken babi Ayu 21