Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 19:20-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi,Da ƙyar na kuɓuta.

21. Ku abokaina ne! Ku ji tausayina!Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa.

22. Me ya sa kuke ɓata mini rai kamar yadda Allah ya yi?Azabar da kuka yi mini har yanzu ba ta isa ba?

23. “Da ma a ce wani zai rubuta abin da nake faɗa,Ya rubuta shi a littafi!

24. Ko kuwa ya zana kalmomina da kurfi a kan dutse,Ya rubuta su don su tabbata har abada!

25. Amma na sani akwai wani a SamaniyaWanda a ƙarshe zai zo ya tsaya mini.

26. Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata,A wannan jiki zan ga Allah.

Karanta cikakken babi Ayu 19