Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 19:13-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. “'Yan'uwana sun yashe ni,Na zama baƙo ga idon sanina.

14. Dangina da abokaina sun tafi.

15. Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni.Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa.

16. Sa'ad da na kira barana, ba ya amsawa,Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni.

17. Har matata ma ba ta iya jurewa da ɗoyin numfashina,'Yan'uwana maza kuwa ba su ko zuwa kusa da ni.

18. 'Yan yara sukan raina ni su yi mini dariya sa'ad da suka gan ni.

19. Aminaina na kusa sukan dube ni, duban ƙyama,Waɗanda na fi ƙaunarsu duka sun zama maƙiyana.

20. Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi,Da ƙyar na kuɓuta.

Karanta cikakken babi Ayu 19