13. “'Yan'uwana sun yashe ni,Na zama baƙo ga idon sanina.
14. Dangina da abokaina sun tafi.
15. Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni.Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa.
16. Sa'ad da na kira barana, ba ya amsawa,Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni.