Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 19:10-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Ya mammangare ni,Ya tumɓuke sa zuciyata,Ya bar ni in yi yaushi, in mutu.

11. Allah ya zaburo mini da fushi,Ya maishe ni kamar mafi mugunta daga cikin maƙiyansa.

12. Ya aiko da rundunar sojansa don ta fāɗa mini,Suka haƙa ramummuka kewaye da alfarwata inda za su yi kwanto.

13. “'Yan'uwana sun yashe ni,Na zama baƙo ga idon sanina.

14. Dangina da abokaina sun tafi.

15. Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni.Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa.

16. Sa'ad da na kira barana, ba ya amsawa,Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni.

Karanta cikakken babi Ayu 19