1. Ayuba ya amsa.
2. “Me ya sa kuke azabta ni da maganganu?
3. A kowane lokaci kuna wulakanta ni,Ba kwa jin kunya yadda kuke zagina.
4. Da a ce ma na aikata abin da yake ba daidai ba ne,Da me ya cuce ku?
5. Tsammani kuke kun fi ni ne,Kuna ɗauka cewa wahalar da nake shaTa tabbatar ni mai laifi ne.